Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, shafin yada labarai na Al-Watan ya bayar da rahoton cewa, an gudanar da wannan gagarumin biki ne da daya daga cikin cibiyoyin horar da haddar kur’ani da ke kauyen Sharshaba da ke garin “Zafti” da ke lardin Gharbia na kasar Masar.
Samari da ‘yan mata wadanda suka haddace kur’ani a sanye da atamfa mai launin rawaya da tufafi na musamman sun hallara a daya daga cikin manyan zaurukan kauyen bayan sun zagaya manyan tituna.
Mazauna kauyen kuma sun dauki wadannan mahardar Alkur’ani a matsayin abin alfahari ta hanyar samar da dakin taro.
"Sheikh Yaser Habib" daya daga cikin wadanda suka shirya wannan biki ya bayyana cewa: A duk shekara ana gudanar da bikin karrama mahardatan kur'ani, ta yadda ma'abota haddar al-Qur'ani su fara tafiya a hanyar da jama'ar gari suka kewaye su, wanda hakan wata hanya ce ta karrama su. kuma da ita ake gudanar da ita da nufin daukaka tarbiyyar wadannan maluman Al-Qur'ani.
Sannan kuma ya dauki haddar Alkur'ani a matsayin wata babbar daraja, sannan ya ce: Allah madaukaki ya daukaka darajar wadanda suka haddace lafuzzan wahayi.
Sheikh Yaser Habib ya ci gaba da cewa: Yara da matasa da aka karrama a wannan biki sun kasance daga shekaru 6 zuwa 13, da kuma bayar da takardun shaida da kyaututtuka a gaban "Mahmoud Abdullah Abu Hossein" dan majalisar dattawan Masar. , ya kasance daya daga cikin sassan wannan bikin.